A Najeriya,wasu 'ƴan bindiga sun mamaye al'ummomi karamar hukumar Borgu ta jihar Neja, inda suka sace wasu masu ibada da ba a tantance adadinsu ba jim kadan bayan sallar Juma'a. Maharan sun afkawa garuruwan Dekara, Gidan Zana, Sabon Gida da Masaka, a cewar mazauna yankin da kuma dan majalisar tarayya mai wakiltar yankin Jafar Muhammad Shetiman Borgu.
2026-08-22 19:39:50