A ranar asabar da ta gabata ne, wasu masu fafufutuka da suka haɗa da ƴan siyasa, fararen hula, masana dokoki da dai sauransu da ke zaune a ƙetare, suka ƙaddamar da wani ƙawance da ake kira da suna ADS, (Alliance des Domocrates du Sahel) wanda babbar manufarsa ita ce sake dawo da tsarin dimokuraɗiyya a ƙasashen yankin Sahel da yanzu haka ke ƙarƙashin mulkin soji da suka hada da Burkina Faso, Mali da kuma Nijar.
2026-05-11 06:59:44