A jiya Juma'a, wakiliyar Ministar Faransa mai kula da Sojojin da Harkokin Tsoffin Sojoji, Alice Rufo, ta isa Sétif na ƙasar Algeria da nufin sake farfado da daddadiyar huldar dangantaka ta fuskar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu. Uwargida Alice Rufo ta halarci bikin tunawa da kisan kiyashin Sétif a Algeria, wanda ya fara a ranar 8 ga Mayu, 1945, wanda aka bayyana ta yada sojojin mulkin mallaka karkashin Faransa suka nuna rashin tausayi wajen aikata ba dai dai a wancan lokaci.
2026-05-09 13:15:34